Skip to main content

Wayayyar mace

 WAYAYYAR MACE.

-

❝Wayayyiyar mace itace macen da ta iya tarairayar mijinta a lokacin da yake cikin halin ƙuncin rayuwa ko wata fargaba, ba wacce za ta sake cusa masa wani baƙin cikin akan baƙin cikin da ya shigo dashi cikin gida ba. Da yawan matan da suka yi wayewar addini, ko kuma suka san martabar aurensu, da zarar sunga ran mazajensu su ya ɓaci, to sun san salon da za subi domin su kwantar musu da hankali, su yaye musu wannan baƙin cikin da suka shigo dashi cikin gida❞

-

"Ba wai sai lallai ilmin addini ko na rayuwa bane kaɗai yake zamtowa wayewa, ki san yadda za ki farantawa mai gidanki rai a lokacin da ransa ya ɓaci wannan ma wayewa ce ta musamman"

-

"Da yawan wasu ma'auratan basu san yadda za su gusarwa da junansu wani baƙin cikin da yake damun ɗayan sashensu ba, za ka samu wata matar bata iya sanyayawa mijinta rai ba a lokacin da taga ransa a ɓace, haka nan za ka sami wani mijin bai iy sanyayawa ran matarsa ba a lokacin da yaga ranta a ɓace, wanda kuma hakan yakan iya kawo naƙasu da rashin jin daɗin zamantakewar aure a tsakaninsu"

-

Allah ta'ala yasa mu dace baki ɗaya.






Comments

Popular posts from this blog

Kotu Ta Bada Umarnin kwace littatafan Abduljabar Kabara Da kuma bayar da umarnin rushe masallatansa

 Kotu Ta Bada Umarnin kwace littatafan Abduljabar Kabara Da kuma bayar da umarnin rushe masallatansa. ko da yake har yanzu kotun bata bayyana ranar da za a rataye fitaccen malamin ba. Kotu a jihar Kano da ke Najeriya, ta yankewa fitaccen malamin nan Abduljabbar Nasiru Kabara hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan samunsa da laifin tayar da zaune tsaye da kuma bata suna ga fiyayyen halitta (S.A.W) Daga nan kuma ya yanke wa wanda ake tuhuma hukunci kan tuhume-tuhumen da ake yi masa. An dai gurfanar da Kabara a gaban kotu kan lamarin da ya shafi kalaman batanci ga Manzon Allah (SAW), matakin da ke iya tada zaune tsaye. A watan Yulin 2021 ne gwamnatin jihar Kano ta gurfanar da shi. Abduljabbar dai ya bayyana gaban kotun cikin nutsuwar da ba’a taba gani ba tun bayan fara shari’ar, yana mai ban carbi tare da sauraron karar. Da aka tambaye shi ko yana da wani abu da zai fada wa kotun, Barista Aminu Ado Abubakar, wanda ya tsaya a matsayin lauyan wanda ake kara, ya roki kotun da ta yi wa wan...

Peter Obi Bazai Iya Lashe Zaben 2023 ba___Chewar Gwamnan Jihar Anambra

 Peter Obi ba zai iya lashe zaɓen 2023 ba, Cewar Gwamnan Anambra Soludo. Gwamnan jihar Anambra Chukwuma Soludo, ya bayyana cewa jam’iyyar Labour (LP) na Peter Obi ba za ta lashe zaben 2023 ba.”  Soludo ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a wata kasida mai suna ‘Tarihi ya nuna kuma ba zan yi shiru ba (Sashe na 1).  Ya ce: “Bari ya bayyana sarai: Peter Obi ya san cewa ba zai iya ba kuma ba zai yi nasara ba. Ya san wasan da yake yi, shi ma ya sani, kuma ya san na sani.   “Wasan da yake bugawa shine  babban dalilin da yasa bai koma APGA ba. Gaskiyar mugunyar gaskiya (wasu kuma za su ce, Allah Ya kiyaye) ita ce, akwai mutane biyu jam'iyun da ke neman takarar shugaban ƙasa, Jam'iyyun sune kamaraka APC da PDP sauran wasan kwaikwayo ne mai ban sha'awa.” Gwamanan ya ƙara da cewa ya riga da ya faɗa masa ra’ayinsa, Lallai babu wata tafarki ingantacciya gare shi a kusa da mukamai biyu na farko, kuma idan ba a kula ba, ba zai ma kusanci matsayi na uku ba ko da a wurin ƙ...

Cikin Hotuna

Hotuna: Comrd Bashir Yau Bashowa Hotunan Yadda: Maigirma Gwamnan Jihar Katsina Alh Aminu Bello Masari, ya Jagoranchi taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC, wanda  ya gudana yau Lahadi a dakin taro na gidan Gwamnati.